Mene Ne Hukuncin Yi Wa Mace Kaciya?

0
2184

Kaciyar mata a Musulunce ba ta da wani hukunci na a yi, ko kar a yi cikin shari’ar Musulunci.

Saboda duk hadisan dake cikin littattafai kamar su: Sunan na Turmuzi da ragowar littattafai, ba su yi magana kan wajibi ne yin kaciyar ko sunna ba. sun yi bayanin al’ada ce na masu yi a waɗancan lokutan baya, tsari na kiwon lafiya kuma, ya nuna hakan na yin lahani ga ‘ya mace, tunda haka ne kuma, Musulunci na karewa duk wani Musulmi abubuwa guda biyar (5) ciki harda lafiyarsa, “ka ga kuwa bai halatta a yi ba, matsawar akwai cutuwa a ciki”.

Sassa bakwai (7) na jikin ɗan Adam, diyarsu daidai take da diyar rai, domin su ne suke tafiyar da rai da Allah ya busa maka. Sassan su ne kamar haka:

  1. Ido
  2. Kunne
  3. Hanci
  4. Harshe
  5. Wuya
  6. Baya
  7. Al’aura.
A likitance kuma:
Yi wa yarinya mace kaciya kamar rage mata daraja ne, kuma ba wani amfanin yi ma mace kaciya. Kuma yin haka yana sa a hukunta duk wanda ya yi ma ‘yarsa mace kaciya.
labarin da ya wuceYadda Ake Amfani Da Na’urar Gwajin Ciki (Juna Biyu)
Labarin na GabaYadda Ake Taimama
Nine wanda ya samar da wannan manhajar wikiHausa tare da abokaina domin taimaka hausawa wajen samon ilimin cikin harshen Hausa a sauƙaƙe